Irm 13:14-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Zan sa su kara da junansu, iyaye maza da 'ya'yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi, ko juyayi, ko jinƙai ba za su sa in fasa hallaka su duka ba.’ ”

15. Ku kasa kunne, ku ji,Kada ku yi girmankai, gamaUbangiji ya yi magana.

16. Ku girmama Ubangiji Allahnku,Kafin ya kawo duhu,Kafin kuma ƙafafunku su yi tuntuɓea kan dutse, da duhu duhu,Sa'ad da kuke neman haske, sai yamaishe shi duhu,Ya maishe shi duhu baƙi ƙirin.

17. Amma idan ba za ku ji ba,Raina zai yi kuka a ɓoye sabodagirmankanku,Idanuna za su yi kuka ƙwarai, za suzub da hawaye,Domin an kai garken Ubangiji zuwabauta.

18. Ubangiji ya ce wa Irmiya,“Ka faɗa wa sarki da sarauniya,uwarsa, su sauka daga gadonsarautarsu,Domin an tuɓe kyakkyawan rawaninsarautarsu daga kansu.

19. An kulle biranen Negeb,Ba wanda zai buɗe su,Yahuza duka an kai ta zaman dole,Dukanta an kai ta zaman dole.

Irm 13