Fit 35:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai Musa ya tattara dukan taron jama'ar Isra'ila, ya ce musu, “Waɗannan su ne abubuwan da Ubangiji ya umarce ku ku yi.

2. Cikin kwana shida za a yi aiki, amma rana ta bakwai Asabar ce tsattsarka ta Ubangiji ta hutawa sosai. Duk wanda ya yi kowane irin aiki a cikinta, sai a kashe shi.

3. Ba za ku hura wuta a ranar Asabar a wuraren zamanku ba.”

Fit 35