Fit 22:28-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. “Kada ku saɓi Allah, kada kuma ku zagi mai mulkin jama'arku.

29. “Kada ku yi jinkirin fitar da zakar amfanin gonarku ta hatsi da ta abin matsewa.'Ya'yan farinku, maza, kuma za ku ba ni su.

30. Haka kuma za ku yi da 'ya'yan farin shanunku, da na awakinku, da na tumakinku. Ɗan farin zai yi kwana bakwai tare da uwar, amma a rana ta takwas za ku ba ni shi.

31. “Za ku zama keɓaɓɓun mutane a gare ni. Kada ku ci dabbar da naman jeji ya yayyage shi, sai ku jefa wa karnuka.”

Fit 22