Fit 12:26-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

26. Sa'ad da 'ya'yanku suka tambaye ku, ‘Ina ma'anar wannan farilla?’

27. Za ku ce, ‘Hadaya ce ta Idin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra'ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.”’ Sai jama'ar suka durƙusa suka yi sujada.

28. Isra'ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.

Fit 12