Far 48:12-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Yusufu ya kawar da su daga gwiwoyin Isra'ila, ya sunkuyar da fuskarsa har ƙasa a gabansa.

13. Yusufu ya ɗauki su biyu ɗin, Ifraimu a hannunsa na dama zuwa hannun hagun Isra'ila, Manassa kuma a hannunsa na hagu zuwa dama na Isra'ila, ya kawo su kusa da shi.

14. Isra'ila ya miƙa hannunsa na dama, ya ɗora bisa kan Ifraimu wanda yake ƙarami, hannunsa na hagu kuma bisa kan Manassa, yana harɗe da hannuwansa, gama Manassa shi ne ɗan fari.

15. Sai ya sa wa Yusufu albarka, ya ce,“Allah na Ibrahim da Ishaku,Iyayena da suka yi tafiyarsu agabansa,Allah da ya bi da niDukan raina har wa yau, ya sa musualbarka.

Far 48