Far 47:21-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

21. Yusufu ya mai da jama'ar bayi daga wannan kan iyaka na Masar zuwa wancan.

22. Sai gonakin firistoci ne kaɗai bai saya ba, gama firistocin suna da rabo wanda Fir'auna ya yanka musu, da rabon da Fir'auna yake ba su suke zaman gari, sabili da haka ba su sayar da gonakinsu ba.

23. Yusufu ya ce wa jama'ar, “Ga shi, a yau na saya wa Fir'auna ku da gonakinku. Yanzu fa, ga iri dominku, za ku shuka gonakin.

Far 47