Far 42:22-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. Sai Ra'ubainu ya amsa musu, “Ashe, dā ma ban faɗa muku kada ku cuci yaron ba? Amma ba ku saurara ba. To, ga shi fa, ana neman hakkinsa yanzu.

23. Ba su sani ba, ashe, Yusufu yana jinsu, domin akwai tafinta a tsakaninsu.

24. Ya juya waje ɗaya ya yi kuka, sai ya sāke komawa wurinsu ya yi magana da su. Ya ɗauki Saminu daga cikinsu ya ɗaure shi a kan idonsu.

Far 42