29. dukan dukiyarsu, da 'yan ƙananansu, da matansu, wato dukan abin da yake cikin gidajen, suka kwashe.
30. Sai Yakubu ya ce wa Saminu da Lawi, “Kun jawo mini wahala. Kun sa na zama abin ƙi ga Kan'aniyawa da Ferizziyawa mazaunan ƙasar. Mutanena kima ne, in suka haɗa kai suka fāɗa mini, za su hallaka ni, da ni da gidana.”
31. Amma 'ya'yansa suka ce, “Zai mai da ƙanwarmu kamar karuwa?”