Far 24:34-40 Littafi Mai Tsarki (HAU)

34. Ya ce, “Ni baran Ibrahim ne.

35. Ubangiji ya sa wa maigidana albarka ƙwarai, ya kuwa zama babba, ya ba shi garkunan tumaki da na shanu, da azurfa da zinariya, da barori mata da maza, da raƙuma da jakai.

36. Saratu ta haifa wa maigidana ɗa cikin tsufanta, a gare shi kuma ya ba da dukan abin da yake da shi.

37. Maigidana ya rantsar da ni da cewa, ‘Ba za ka auro wa ɗana mace daga cikin 'ya'yan Kan'aniyawa waɗanda nake zaune a ƙasarsu ba,

38. amma ka tafi gidan mahaifina da dangina, ka auro wa ɗana mace.’

39. Sai na ce wa maigidana, ‘Watakila matar ba za ta biyo ni ba.’

40. Amma ya amsa mini ya ce, ‘Ubangiji wanda nake tafiya a gabansa zai aiki mala'ikansa tare da kai, ya arzuta hanyarka, za ka kuwa auro wa ɗana mace daga cikin dangina daga gidan mahaifina.

Far 24