Far 24:34-37 Littafi Mai Tsarki (HAU)

34. Ya ce, “Ni baran Ibrahim ne.

35. Ubangiji ya sa wa maigidana albarka ƙwarai, ya kuwa zama babba, ya ba shi garkunan tumaki da na shanu, da azurfa da zinariya, da barori mata da maza, da raƙuma da jakai.

36. Saratu ta haifa wa maigidana ɗa cikin tsufanta, a gare shi kuma ya ba da dukan abin da yake da shi.

37. Maigidana ya rantsar da ni da cewa, ‘Ba za ka auro wa ɗana mace daga cikin 'ya'yan Kan'aniyawa waɗanda nake zaune a ƙasarsu ba,

Far 24