Far 24:25-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

25. Ta ƙara da cewa, “Muna da isasshen baro da harawa duka, da kuma masauki.”

26. Mutumin ya yi ruku'u ya yi wa Ubangiji sujada,

27. ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji na maigidana Ibrahim, wanda bai daina nuna madawwamiyar ƙaunarsa da amincinsa ga maigidana ba. Ubangiji ya bi da ni har zuwa gidan ɗan'uwan maigidana.”

28. Budurwar ta sheƙa a guje zuwa gida wurin mahaifiyarta ta faɗi waɗannan abubuwa.

Far 24