22. Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa wurin.” Domin haka aka kira sunan garin Zowar.
23. Da hantsi Lutu ya isa Zowar.
24. Sai Ubangiji ya yi ta zuba wa Saduma da Gwamrata wutar kibritu daga sama,
25. ya hallakar da waɗannan birane, da dukan kwarin, da dukan mazaunan biranen, da tsire-tsire.