Ezra 7:27-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na kakanninmu, wanda ya sa a zuciyar sarki ya ƙawata Haikalin Ubangijin da yake a Urushalima.

28. Wanda kuma ya sa na sami tagomashi a wurin sarki, da 'yan majalisarsa, da manyan ma'aikatansa. Na sami ƙarfin hali, gama Ubangiji Allahna yana tare da ni. Sai na tattara manyan mutane na Isra'ila don mu tafi tare.

Ezra 7