Ezra 4:8-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Rehum shugaban sojoji, da Shimshai magatakarda, suka rubuta takardar ƙara a kan Urushalima zuwa Sarki Artashate.

9. Sa'an nan Rehum shugaban sojoji ya rubuta tare da Shimshai magatakarda,da abokansu, da alƙalai, da masu mulkin larduna, da ma'aikatan hukumomi, wato mutanen Farisa, da na Erek, da na Babila, da na Shusha a ƙasar Elam,

10. da sauran al'ummai, waɗanda mai girma, Asnaffar, ya kwaso, ya zaunar da su a biranen Samariya, da sauran wurare na Yammacin Kogi.

11. Ga abin da suka rubuta.“Gaisuwa daga talakawanka, mutane na hayin Kogin zuwa ga sarki Artashate.

12. “Muna sanar da sarki, cewa Yahudawan nan waɗanda suka fito daga gare ka suka zo wurinmu, sun tafi Urushalima, suna sāke gina mugun birnin nan na tawaye, sun fara gina garun, ba da jimawa ba za su gama ginin.

Ezra 4