16. “Ɗan mutum, ka ɗauki sanda, ka rubuta a kansa, ‘Domin Yahuza da magoyan bayansa.’ Ka kuma ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Domin Yusufu, sandan Ifraimu, da dukan mutanen Isra'ila, magoyan bayansa.’
17. Ka haɗa su su zama sanda guda a hannunka.
18. Sa'ad da kuma jama'arka suka ce maka ka nuna musu abin da kake nufi da waɗannan,