21. Amma na damu saboda sunana mai tsarki wanda mutanen Isra'ila suka sa aka ɓata shi a wurin al'ummai inda suka tafi.
22. “Domin haka sai ka faɗa wa mutanen Isra'ila, ni Ubangiji Allah na ce, ‘Ba saboda ku ba ne, ya mutanen Isra'ila, zan yi wani abu, amma saboda sunana mai tsarki wanda kuka ɓata a wurin al'ummai inda kuka tafi.
23. Zan ɗauki fansa saboda sunana mai tsarki, mai girma, wanda aka ɓata a wurin al'ummai, ku kuma kuka ɓata shi a cikinsu. Al'ummai kuwa za su sani ni ne Ubangiji sa'ad da na tabbatar da tsarkina a wurinku a kan idonsu.
24. Zan kwaso ku daga cikin al'ummai, in tattaro ku daga dukan ƙasashe, in kawo ku cikin ƙasarku.