Ez 33:16-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Ba za a tuna da laifofin da ya aikata a dā ba, gama ya aikata adalci da gaskiya, zai rayu.

17. “Amma mutanenka sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce,’ alhali kuwa tasu ce ba daidai ba.

18. Sa'ad da adali ya daina aikata adalci, ya shiga aikata laifi, zai mutu saboda laifinsa.

19. Sa'ad da kuma mugu ya daina aikata mugunta, ya shiga aikata adalci da gaskiya, zai rayu saboda adalcinsa.

20. Amma duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ya mutanen Isra'ila, zan hukunta kowane ɗayanku gwargwadon ayyukansa.”

Ez 33