Ez 32:13-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Zan hallaka dukan dabbobinta da suke bakin ruwa,Ba ƙafar mutum ko ta dabba da za ta ƙara gurɓata ruwa.

14. Zan sa ruwansu ya yi garau,In sa kogunansu su malala kamar mai,Ni Ubangiji Allah na faɗa.

15. Sa'ad da na mai da ƙasar Masar kufai,In raba ƙasar da abin da take cike da shi,Sa'ad da na bugi dukan waɗanda suke cikinta,Daga nan za su sani ni ne Ubangiji.

16. Wannan ita ce waƙar makokin. 'Yan matan al'ummai za su raira wa Masar da jama'arta duka, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

17. A rana ta goma sha biyar ga wata na fari, a shekara ta goma sha biyu, Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce,

18. “Ɗan mutum, ka yi kuka saboda jama'ar Masar. Ka tura su tare da sauran al'umma zuwa lahira wurin waɗanda suka gangara zuwa cikin kabari.

Ez 32