Ez 10:3-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na Haikalin a sa'ad da mutumin ya shiga, girgije kuma ya cika farfajiyar da take can ciki.

4. Ɗaukakar Ubangiji ta tashi daga kan kerubobin zuwa ƙofar Haikalin. Girgije kuwa ya cika Haikalin, hasken zatin Ubangiji ya cika farfajiyar.

5. Sai aka ji amon fikafikan kerubobin a filin da yake can waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa'ad da yake magana.

6. Ya kuwa umarci wanda yake saye da lilin ɗin, ya ce, “Ka ɗibi wuta daga ƙarƙashin ƙafafun da suke tsakanin kerubobin.” Sai ya tafi ya tsaya a gefen ƙafar.

7. Kerub kuwa ya miƙa hannunsa daga tsakanin kerubobi zuwa wurin wutar da take tsakanin kerubobin, ya ɗebo wutar, ya zuba a ahannun mutumin da yake saye da rigar lilin. Shi kuwa ya karɓa, ya fita.

8. Kerubobin suna da hannuwa kamar na 'yan adam a ƙarƙashin fikafikansu.

Ez 10