3. “Alamunsa da girma suke!Al'ajabansa da bantsoro suke!Sarautarsa ta har abada ce,Mulkinsa kuma daga zamani zuwa zamani ne.
4. “Ni, Nebukadnezzar ina cikin gidana, ina nishaɗi a fādata.
5. Sa'ad da nake kwance a gādona, sai na yi mafarki wanda ya tsorata ni. Tunanina da wahayi suka firgitar da ni.
6. Don haka na umarta a kirawo mini dukan masu hikima na Babila don su yi mini fassarar mafarkin.