Dan 3:8-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. A lokacin sai waɗansu Kaldiyawa suka tafi, suka yi ƙarar Yahudawa.

9. Suka ce wa sarki Nebukadnezzar, “Ranka ya daɗe.

10. Kai ne ka yi doka, cewa duk mutumin da ya ji ƙarar ƙaho, da sarewa, da garaya, da goge, da molo, da algaita, da kowane irin abin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe, sai ya fāɗi ƙasa, ya yi sujada ga gunkin zinariya.

11. Duk wanda bai fāɗi ƙasa ya yi sujada ba, za a jefa shi a tanderun gagarumar wuta.

Dan 3