Ayu 38:8-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. “Wa ya yi wa teku iyakaSa'ad da ta tumbatso daga zurfafa?

9. Sa'ad da na suturta ta da gizagizai,Na yi mata maɗauri da duhu ƙirin.

10. Na sa mata iyakoki,Na sa mata ƙyamare da ƙofofi,

11. Na ce mata, ‘Iyakar inda za ki tsaya ke nan,Ba za ki wuce ba.Nan raƙuman ruwanki masu tumbatsa za su tsaya.’

12. “Ayuba, a dukan kwanakinkaKa taɓa umartar wayewar gari,Ko ka sa alfijir ya keto?

13. Da gari ya waye,Ka kawar da muguntar da ake yi da dare?

14. Yakan sāke kamar lakar da take ƙarƙashin hatimi,Yakan rine kamar riga.

Ayu 38