26. Sa'an nan ne mutum zai yi addu'a ga Allah, ya karɓe shi,Ya zo gabansa da murna,Allah zai komar wa mutum da adalcinsa.
27. Zai raira waƙa a gaban jama'a, ya ce, ‘Na yi zunubi. Ban yi daidai ba,Amma ba a sa ni in biya ba.
28. Allah ya fanshe ni daga gangarawa zuwa kabari,Raina kuwa zai ga haske.’
29. “Ga shi kuwa, Allah ya yi dukan waɗannan abubuwa sau biyu, har ma sau uku ga mutum,