10. Hakika shanunsu suna ta hayayyafa,Suna haihuwa ba wahala.
11. 'Ya'yansu suna guje-guje,Suna tsalle kamar 'yan raguna,
12. Suna rawa ana kaɗa garaya,Ana busa sarewa.
13. Suka yi zamansu da salama,Su mutu shiru ba tare da shan wahala ba.
14. Mugaye sukan ce wa Allah ya ƙyale su kurum,Ba su so su san nufinsa game da hanyoyinsu.
15. Suna tsammani ba amfani a bauta wa Allah,Ko a yi addu'a gare shi domin samun wata fa'ida.
16. Sukan ce ta wurin ƙarfinsu ne suka yi nasara,Amma ban yarda da irin tunaninsu ba.