Ayu 16:7-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Ka gajiyar da ni, ya Allah,Ka shafe iyalina.

8. Ka kama ni, kai maƙiyina ne.Na zama daga fata sai ƙasusuwa,Mutane suka ɗauka, cewa wannan ya tabbatar ni mai laifi ne.

9. Allah ya kakkarya gaɓoɓina da fushinsa,Yana dubana da ƙiyayya.

10. Mutane sun buɗe baki don su haɗiye niSuna kewaye ni suna ta marina.

11. Allah ya bashe ni ga mugaye.

Ayu 16