Ayu 16:5-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Da sai in ba ka shawara ta ƙarfafawa,In yi ta yi maka maganar ta'azantarwa.

6. “Amma ba abin da zan faɗa wanda zai taimaka,Yin shiru kuma ba zai raba ni da azaba ba.

7. Ka gajiyar da ni, ya Allah,Ka shafe iyalina.

8. Ka kama ni, kai maƙiyina ne.Na zama daga fata sai ƙasusuwa,Mutane suka ɗauka, cewa wannan ya tabbatar ni mai laifi ne.

9. Allah ya kakkarya gaɓoɓina da fushinsa,Yana dubana da ƙiyayya.

10. Mutane sun buɗe baki don su haɗiye niSuna kewaye ni suna ta marina.

11. Allah ya bashe ni ga mugaye.

12. Dā ina zamana da salama,Amma Allah ya maƙare ni,Ya fyaɗa ni ƙasa ya ragargaza ni.Allah ya maishe ni abin bārata.

Ayu 16