1. Ayuba ya amsa.
2. “Aha! Ashe, kai ne muryar jama'a,Idan ka mutu hikima ta mutu ke nan tare da kai.
3. Amma ni ma ina da hankali gwargwado, kamar yadda kake da shi,Ban ga yadda ka fi ni ba.Kowa ya san sukan abin da ka faɗa.
4. Har abokaina ma, suna ta yi mini dariya yanzu,Suna ta dariya ko da yake ni adali ne marar laifi,Amma akwai lokacin da Allah ya amsa addu'o'ina.
5. Ba ka shan wahalar kome, duk da haka ka maishe ni abin dariya.Ka bugi mutumin da yake gab da fāɗuwa.
12-13. “Tsofaffi suna da hikima,Amma Allah yana da hikima da iko.Tsofaffi suna da tsinkaya,Amma Allah yana da tsinkaya da ikon aikatawa.