1. Ayuba ya amsa.
10. Allah shi ne yake bi da rayukan talikansa.Numfashin dukan mutane kuwa a ikonsa yake.
11. Amma kamar yadda harsunanku suke jin daɗin ɗanɗanar abinci,Haka nan kuma kunnuwanku suke jin daɗin sauraren kalmomi.
12-13. “Tsofaffi suna da hikima,Amma Allah yana da hikima da iko.Tsofaffi suna da tsinkaya,Amma Allah yana da tsinkaya da ikon aikatawa.