A.m. 3:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. To, Bitrus da Yahaya suna tafiya Haikali a lokacin addu'a, da ƙarfe uku na yamma,

2. sai ga wani mutum da aka haifa gurgu, ana ɗauke da shi. Kowace rana kuwa akan ajiye shi a ƙofar Haikali, wadda ake kira Ƙawatacciyar Ƙofa, don ya roƙi sadaka ga masu shiga Haikali.

3. Da ganin Bitrus da Yahaya suna shiga Haikalin, ya roƙe su sadaka.

4. Bitrus kuwa ya zuba masu ido, tare da Yahaya, ya ce, “Dube mu.”

5. Sai kuwa duk hankalinsa ya koma a kansu, da tsammanin samun wani abu a gunsu.

6. Amma Bitrus ya ce, “Kuɗi kam, ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. Da sunan Yesu Almasihu Banazare, yi tafiya.”

A.m. 3