A.m. 21:12-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Da muka ji haka, mu da waɗanda suke wurin muka roƙi Bulus kada ya je Urushalima.

13. Sai Bulus ya amsa ya ce, “Me ke nan kuke yi, kuna kuka kuna baƙanta mini rai? Ai, ni a shirye nake, ba wai a ɗaure ni kawai ba, har ma a kashe ni a Urushalima saboda sunan Ubangiji Yesu.”

14. Da dai ya ƙi rarrasuwa, muka yi shiru, muka ce, “Ubangiji ya yi yadda ya so.”

15. Bayan 'yan kwanakin nan muka shirya muka tafi Urushalima.

16. Waɗansu masu bi daga Kaisariya suka rako mu, suka kawo mu wurin Manason, mutumin Kubrus, wani daɗaɗɗen mai bi, wanda za mu sauka a gunsa.

17. Da muka zo Urushalima, 'yan'uwa suka karɓe mu da murna.

A.m. 21