A.m. 17:7-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. har ma Yason ya sauke su! Dukansu kuwa suna saɓa dokokin Kaisar, suna cewa wani ne sarki, wai shi Yesu.”

8. Da mutanen gari da mahukunta suka ji wannan, hankalinsu ya tashi.

9. Ba su sake su ba, sai da suka karɓi kuɗin lamuni a hannun Yason da sauransu.

10. Nan da nan kuwa da dare ya yi, 'yan'uwa suka sallami Bulus da Sila su tafi Biriya. Da suka isa can kuma suka shiga majami'ar Yahudawa.

11. To, waɗannan Yahudawa kam, sun fi na Tasalonika dattaku, domin sun karɓi Maganar hannu biyu biyu, suna ta nazarin Littattafai kowace rana, su ga ko abin haka yake.

A.m. 17