34. [Amma Sila ya ga ya kyautu shi ya zauna a nan.]
35. Bulus da Barnaba kuwa suka dakata a Antakiya, suna koyarwa suna kuma yin bisharar Maganar Ubangiji, tare da waɗansu ma da yawa.
36. An jima, Bulus ya ce wa Barnaba, “Bari yanzu mu koma mu dubo 'yan'uwa a kowane gari da muka sanar da Maganar Ubangiji, mu ga yadda suke.”
37. Barnaba kuwa ya so su tafi da Yahaya, wanda ake kira Markus.