2 Tar 32:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Bayan waɗannan abubuwa, da waɗannan ayyukan aminci, sai Sennakerib, Sarkin Assuriya, ya kawo wa Yahuza yaƙi, ya kafa sansani kewaye da garuruwa masu garu, yana zaton zai ci su da yaƙi su zama nasa.

2. Da Hezekiya ya ga Sennakerib ya zo da nufin ya yi yaƙi da Urushalima,

3. sai ya yi shawara shi da jarumawansa da manyan mutanensa, su datse ruwan da yake fitowa daga maɓuɓɓugar da suke bayan birni, suka kuwa taimake shi.

4. Don haka mutane da yawa suka taru suka daddatse dukan maɓuɓɓugai da rafuffuka da suke gudu cikin ƙasar, suna cewa, “Bari mu hana sarakunan Assuriya samun ruwa idan sun iso Urushalima.”

2 Tar 32