2 Tar 31:16-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. da su kuma waɗanda aka rubuta bisa ga asali, 'yan samari masu shekara uku zuwa sama, duk dai waɗanda za su shiga Haikalin Ubangiji don yin hidima, kamar yadda aka tsara, bisa ga matsayinsu yadda aka karkasa su.

17. Aka kuma rubuta firistoci bisa ga gidajen kakanninsu, na wajen Lawiyawa kuwa, tun daga mai shekara ashirin zuwa sama, bisa ga matsayinsu, ta yadda aka karkasa su.

18. Aka rubuta firistoci tare da dukan ƙananan 'ya'yansu, da matansu, da 'ya'yansu mata da maza, dukansu gaba ɗaya, gama da zuciya ɗaya suka tsarkake kansu.

19. Akwai mutane a garuruwa da yawa waɗanda aka sa don su rarraba wa 'ya'yan Haruna, firist, maza kuwa, waɗanda suke zaune a gonaki na ƙasar garuruwansu su ba kowane namiji da aka rubuta na Lawiyawa, nasa rabo.

2 Tar 31