2 Tar 20:28-32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

28. Suka shigo Urushalima da molaye da garayu, da ƙaho zuwa Haikalin Ubangiji.

29. Tsoron Ubangiji kuwa ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa'ad da suka ji Ubangiji ya yi yaƙi da maƙiyan Isra'ilawa.

30. Mulkin Yehoshafat kuwa ya sami salama, gama Allahnsa ya ba shi hutawa a kowane gefe.

31. Yehoshafat ya yi mulkin Yahuza. Yana da shekara talatin da biyar sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan tsohuwarsa Azuba, 'yar Shilhi.

32. Ya bi tafarkin tsohonsa, Asa, bai kuwa kauce ba, ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji.

2 Tar 20