3. “Ka faɗa wa Rehobowam ɗan Sulemanu, Sarkin Yahuza, da dukan Isra'ilawa da suke a Yahuza da Biliyaminu, ka ce,
4. ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, kada ku yi yaƙi da 'yan'uwanku, kowa ya komo alfarwarsa, gama wannan al'amari daga gare ni yake.’ ” Suka kuwa ji maganar Ubangiji, suka koma, ba su tafi yaƙi da Yerobowam ba.
5. Rehobowam ya zauna a Urushalima, ya kuwa gina birane masu kagara a Yehuza.
6. Ya gina Baitalami, da Itam, da Tekowa,
7. da Bet-zur, da Soko, da Adullam,