18. Ya faru daidai yadda annabi Elisha ya ce wa sarki, “Za a sayar da mudu biyu na sha'ir, da mudu na lallausan gari a bakin shekel ɗaya ɗaya gobe war haka a ƙofar birnin Samariya.”
19. Dogarin ya ce wa Elisha, “Ko da Ubangiji da kansa zai buɗe tagogin sama, wannan abu zai yiwu ke nan?”Elisha kuwa ya ce, “Za ka gani da idanunka amma ba za ka ci ba.”
20. Haka kuwa ya zama gama mutane suka tattake shi a ƙofar har ya mutu.