2 Sar 20:7-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Sai Ishaya ya ce, “Ku yi masa farsa da ɓaure, marurun zai warke.”

8. Hezekiya kuwa ya ce wa Ishaya, “Mece ce alama, cewa Ubangiji zai warkar da ni har in haura zuwa Haikalin Ubangiji a rana ta uku?”

9. Sai Ishaya ya ce, “Wannan ita ce alama daga wurin Ubangiji, Ubangiji zai cika alkawarin da ya yi. Ƙaƙa kake so, inuwa ta yi gaba da taki goma, ko kuwa ta yi baya da taki goma?”

2 Sar 20