2 Sam 7:27-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

27. Gama kai, ya Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, kai ne ka sanar wa ni bawanka, cewa, za ka sa gidana ya kahu, saboda haka ni bawanka na sami ƙarfin halin yin wannan addu'a a gare ka.

28. “Yanzu kuwa, ya Ubangiji Allah, kai ne Allah, kana cika alkawarinka ko yaushe. Ka kuwa yi wa bawanka alkawari mai girma.

29. Ka yarda da farin ciki ka sa wa gidan bawanka albarka domin gidansa ya dawwama a gabanka har abada, gama kai ne ka faɗa, ya Ubangiji Allah. Ka sa albarkarka ta tabbata a gidan bawanka har abada.”

2 Sam 7