2 Sam 24:1-2 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji kuwa ya husata da Isra'ilawa. Ya kuwa zuga Dawuda a kansu, ya ce, “Tafi ka ƙidaya jama'ar Isra'ila da ta Yahuza.”

2. Sai sarki ya ce wa Yowab da shugabannin sojojin su tafi cikin dukan kabilan Isra'ila, tun daga Dan har zuwa Biyer-sheba, su ƙidaya mutanen don ya san yawansu.

2 Sam 24