44. “Ka cece ni daga jama'ata mai tawaye,Ka sa in yi mulkin al'ummai,Mutanen da ban san su ba sun zama bayina.
45. Baƙi sun zo suna rusuna mini,Sa'ad da suka ji ni suka yi mini biyayya.
46. Zuciyarsu ta karai,Suka fito daga kagararsu suna rawar jiki.
47. “Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga mai tsaronsa!Allah ne ƙaƙƙarfan Mai Cetona! Ku yi shelar girmansa!
48. Ya ba ni nasara a kan abokan gabana,Ya sa mutane a ƙarƙashin mulkina,