2 Sam 14:26-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

26. Sa'ad da ya yi aski yakan auna nauyin gashin kansa, nauyin yakan kai wajen shekel ɗari biyu. Gama a ƙarshen kowace shekara yake aski, sa'ad da gashin ya yi masa nauyi.

27. Aka haifa wa Absalom 'ya'ya uku maza da 'ya mace guda, sunanta Tamar, ita kuwa kyakkyawa ce.

28. Absalom ya yi shekara biyu cif a Urushalima, amma bai sami izinin ganin sarki ba.

29. Sai Absalom ya aika a kira masa Yowab don ya aike shi wurin sarki, amma Yowab ya ƙi zuwa. Ya kuma sāke aikawa, Yowab kuwa ya ƙi zuwa.

30. Sai ya ce wa barorinsa, “Ga Yowab yana da gonar sha'ir kusa da tawa, ku tafi, ku sa mata wuta.” Barorin Absalom kuwa suka tafi suka sa wa gonar wuta.

31. Yowab kuwa ya tashi ya tafi wurin Absalom har gidansa, ya ce masa, “Don me barorinka suka sa wa gonata wuta?”

2 Sam 14