1 Tar 2:16-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. 'Yan'uwansu mata kuwa su ne Zeruya da Abigail.'Ya'yan Zeruya, maza, su ne Abishai, da Yowab, da Asahel, su uku ke nan.

17. Abigail ta haifi Amasa. Mahaifin Amasa shi ne Yeter daga zuriyar Isma'ilu.

18. Azuba, matar Kalibu ɗan Hesruna ta haifa masa 'ya'ya maza. Matarsa Yeriyot kuma ta haifi 'ya'ya maza, su ne Yesher, da Shobab, da Ardon.

19. Sa'ad da Azuba ta rasu sai Kalibu ya auri Efrata wadda ta haifa masa Hur.

1 Tar 2