1 Tar 19:15-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Da Ammonawa suka ga Suriyawa sun gudu, su ma suka gudu daga gaban Abishai, ɗan'uwan Yowab, suka shiga birni. Sa'an nan Yowab ya komo Urushalima.

16. Da Suriyawa suka ga Isra'ilawa sun ci su da yaƙi sai suka aiki manzanni suka kira Suriyawa waɗanda suke hayin kogi. Shobak shugaban sojojin Hadadezer ne yake shugabantarsu.

17. Sa'ad da aka faɗa wa Dawuda, sai ya tattara Isra'ilawa duka ya haye Urdun, ya zo wurinsu, ya jā dāga don ya yi yaƙi da su. Aka fara gabza yaƙi,

1 Tar 19