11. Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan ga Ubangiji, tare da azurfa da zinariya waɗanda ya kwaso daga al'umman da ya ci, wato Edom, da Mowab, da mutanen Ammon, da na Filistiya, da na Amalek.
12. Abishai ɗan Zeruya kuma ya ci nasara a kan Edomawa, mutum dubu goma sha takwas (18,000) a Kwarin Gishiri.
13. Sai ya sa ƙungiyoyin sojoji a Edom, dukan Edomawa kuma suka zama bayin Dawuda. Ubangiji kuwa ya taimaki Dawuda duk inda ya tafi.
14. Da haka Dawuda ya yi mulki bisa dukan Isra'ila. Ya yi wa dukan jama'arsa adalci da gaskiya.
15. Yowab ɗan Zeruya shi ne shugaban sojoji, Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubuci.