1 Tar 15:3-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Saboda haka Dawuda ya tattara Isra'ilawa duka a Urushalima don a kawo akwatin alkawarin Ubangiji a wurinsa, inda aka riga aka shirya masa.

4. Dawuda kuma ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya, tare kuma da Lawiyawa.

5. Waɗanda aka tattaro ke nan, daga iyalin Kohat su ɗari da shirin ne. Uriyel shi ne shugabansu.

6. Daga iyalin Merari su ɗari biyu da ashirin, Asaya ne shugabansu.

7. Daga iyalin Gershon ɗari da talatin, Yowel ne shugabansu.

8. Daga iyalin Elizafan ɗari biyu, Shemaiya ne shugabansu.

1 Tar 15