1 Sar 15:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A shekara ta goma sha takwas ta sarautar sarki Yerobowam ɗan Nebat, Abaija ya sarauci mutanen Yahuza.

2. Ya yi mulki shekara uku a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Ma'aka, 'yar Absalom, wato kakarsa.

3. Shi kuma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Bai yi aminci ga Ubangiji Allahnsa sosai, kamar yadda kakansa, Dawuda, ya yi ba.

1 Sar 15