1 Sar 11:34-37 Littafi Mai Tsarki (HAU)

34. Duk da haka ba zan karɓe sarauta duka daga hannunsa ba, amma zan bar shi ya yi mulki muddin ransa saboda bawana Dawuda, wanda na zaɓa, wanda ya kiyaye umarnaina da dokokina.

35. Amma zan karɓe mulki daga hannun ɗansa in ba ka, zan ba ka kabila goma.

36. Duk da haka zan ba ɗansa kabila guda, domin bawana Dawuda ya kasance da fitila kullum a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa sunana.

37. Zan sa ka yi mulki a kan duk abin da ranka yake bukata, za ka zama Sarkin Isra'ila.

1 Sar 11