24. Sa'an nan sai ƙarshen, sa'ad da zai mayar wa Allah Uba mulki, bayan ya shafe dukkan sarauta da mulki da iko.
25. Domin kuwa lalle ne ya yi mulki, har ya take dukkan maƙiyansa.
26. Magabciyar ƙarshe da za a shafe, ita ce mutuwa.
27. “Gama Allah ya sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa.” Amma da aka ce, “An sarayar da kome karƙashin ikonsa” a fili yake shi wannan da ya sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa ɗin, a keɓe yake.